fidelitybank

Wani sabon rikici ya sake ɓarkewa a Jigawa

Date:

Rikici ya sake ɓarkewa tsakanin wasu ƙauyuka biyu da ke ƙaramar hukumar Miga a jihar Jigawa, da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Wannan na zuwa ne mako ɗaya bayan irin wannan rikici wanda ya haifar da asarar rayukan mutum tara.

Mazauna yankin sun shaida wa BBC cewa rikicin – wanda ake yi wa kallon na ramuwar gayya – tsakanin ƙauyukan Gululu, da Gidan Nagare da kuma Ƴan kunama ya sake ɓarkewa ne a daren Juma’ar nan.

Shugaban ƙaramar hukumar Jahun, Jamilu Danmalam ya tabbatar wa BBC cewa maharan sun kashe mutum 11.

Haka nan mazanuna yankin sun ce an ƙona ƙona gidaje da kuma kashe dabbobi a lokacin harin.

Sai dai har yanzu ba a tantance yawan mutanen da suka samu raunuka ba.

Yanzu haka an kai waɗanda suka samu raunuka asibiti a ƙaramar hukumar Jahun da kuma Kano inda za a yi musu magani.

Jigawa na daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ta fi kasancewa cikin zaman lafiya a baya-bayan nan, sai dai ta daɗe tana fama da rikice-rikice na manoma da makiyaya.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp