Rikici ya sake ɓarkewa tsakanin wasu ƙauyuka biyu da ke ƙaramar hukumar Miga a jihar Jigawa, da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Wannan na zuwa ne mako ɗaya bayan irin wannan rikici wanda ya haifar da asarar rayukan mutum tara.
Mazauna yankin sun shaida wa BBC cewa rikicin – wanda ake yi wa kallon na ramuwar gayya – tsakanin ƙauyukan Gululu, da Gidan Nagare da kuma Ƴan kunama ya sake ɓarkewa ne a daren Juma’ar nan.
Shugaban ƙaramar hukumar Jahun, Jamilu Danmalam ya tabbatar wa BBC cewa maharan sun kashe mutum 11.
Haka nan mazanuna yankin sun ce an ƙona ƙona gidaje da kuma kashe dabbobi a lokacin harin.
Sai dai har yanzu ba a tantance yawan mutanen da suka samu raunuka ba.
Yanzu haka an kai waɗanda suka samu raunuka asibiti a ƙaramar hukumar Jahun da kuma Kano inda za a yi musu magani.
Jigawa na daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ta fi kasancewa cikin zaman lafiya a baya-bayan nan, sai dai ta daɗe tana fama da rikice-rikice na manoma da makiyaya.