Alamu masu karfi na nuni da cewa, ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Dr. Chris Ngige, zai bayyana tsayawa takarar shugaban kasa a ranar Talata 19 ga Afrilu, 2022.
Da yake amsa kiraye-kirayen da magoya bayan sa na jamâiyyar APC suka yi wanda da suka yi dafifi a filin jirgin sama na Akanu Ibiam, Enugu, domin tarbarsa, Ngige, ya yi alkawarin amsa bukatarsu a ranar Talata mai zuwa.
Ya lura cewa shiyyar Kudu maso Gabas ta kasance yanki daya tilo a Najeriya da bai dandana romon demokradiyyar shugabancin kasar ba.
Ngige, wanda ya bayyana halartan taron a matsayin âAster Ambushâ, ya ce, ya samu irin wannan kira daga âyanâuwansa a baya, inda ya tabbatar da cewa zai yi magana a wannan karon.
Ya gayyace su zuwa ranar Talata, domin samun amsa, inda ya nuna cewa, ya yi tuntubar juna sosai.
Tun da farko, kakakin kungiyar, Tony Chime, ya shaidawa Ngige cewa, sun zo filin jirgin ne, domin rokonsa ya tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2023.
Chime ya ce, bukatarsu ta dogara ne akan kyawawan bayanan da ya samu a lokacin da yake Gwamnan Jihar Anambra, kuma a yanzu yana Ministan Tarayyar Najeriya.