fidelitybank

Wani jirgin kasa ya kuma gaucewa a Abuja

Date:

Kasa da mako guda bayan da jirgin kasa da ke zirga-zirga tsakanin Itakpe zuwa Warri, a daidai garin Warri, wani jirgin kasan ya goce a Abuja.

Rahotanni na cewa jirgin ya goce ne a unguwar Kubwa da tsakar ranar Juma’a lamarin da ya rutsa da daruruwan fasinjojin da ke cikin jirgin.

Najib Jibril, wani fasinja ne da ke cikin wani jirgin kasa da ya taso daga Abuja zai tafi Kaduna. Ya shaida wa BBC cewa gocewar ta hana nasu jirgin wucewa.

“Ni da wasu fasinjoji muna cikin jirgin da zai kai mu Kaduna, sai muka isa tashar Kubwa inda kamar yadda aka saba, jirginmu ya tsaya yana jiran wanda ya taso daga Kaduna yazo ya wuce.”

Bayan wani lokaci suna jira, sai jirgin da ya taso daga Kaduna ya isa wurin da suke jira.

Fasinjan ya ce, “Yayin da muke jira, sai kwatsam kan da ke jan taragun jirgin ya goce, kuma tun da taragun ba su gama wucewa baki dayansu ba, sai ya kasance sun hana namu jirgin wucewa.”

Sai dai babu bayani kan dalilin da ya janyo gocewar jirgin kasan, amma an ga fasinjoji na yawo a wurin da jirgin ya lalace.

Wata majiya a ma’aikatar Sufuri ta Najeriya ta tabbatar wa BBC aukuwar hadarin.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na Æ™arÆ™ashin Æ´an Bindiga – ÆŠan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan Æ´ansanda mai kula da sashen kai É—auki na...

INEC za ta bai wa É—aurarru damar kaÉ—a Æ™uri’a a lokacin zaÉ“uka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

ÆŠaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon É—an takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaÉ—i mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaÉ—i...
X whatsapp