Kasa da mako guda bayan da jirgin kasa da ke zirga-zirga tsakanin Itakpe zuwa Warri, a daidai garin Warri, wani jirgin kasan ya goce a Abuja.
Rahotanni na cewa jirgin ya goce ne a unguwar Kubwa da tsakar ranar Juma’a lamarin da ya rutsa da daruruwan fasinjojin da ke cikin jirgin.
Najib Jibril, wani fasinja ne da ke cikin wani jirgin kasa da ya taso daga Abuja zai tafi Kaduna. Ya shaida wa BBC cewa gocewar ta hana nasu jirgin wucewa.
“Ni da wasu fasinjoji muna cikin jirgin da zai kai mu Kaduna, sai muka isa tashar Kubwa inda kamar yadda aka saba, jirginmu ya tsaya yana jiran wanda ya taso daga Kaduna yazo ya wuce.”
Bayan wani lokaci suna jira, sai jirgin da ya taso daga Kaduna ya isa wurin da suke jira.
Fasinjan ya ce, “Yayin da muke jira, sai kwatsam kan da ke jan taragun jirgin ya goce, kuma tun da taragun ba su gama wucewa baki dayansu ba, sai ya kasance sun hana namu jirgin wucewa.”
Sai dai babu bayani kan dalilin da ya janyo gocewar jirgin kasan, amma an ga fasinjoji na yawo a wurin da jirgin ya lalace.
Wata majiya a ma’aikatar Sufuri ta Najeriya ta tabbatar wa BBC aukuwar hadarin.