fidelitybank

Wani jigo a PDP ya sauya sheka zuwa APC

Date:

Gabanin zaben 2023, Alhaji Sahabi Bojo-Bodinga daya daga cikin jiga-jigan dattijan jam’iyyar PDP a jihar Sokoto ya sauya sheka zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Bojo-Bodinga ya samu tarba daga shugaban jam’iyyar APC na jihar, Sanata Aliyu Wamakko (APC-Sokoto ta Arewa), a gidansa da ke Sokoto ranar Juma’a.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka raba wa manema labarai a Sokoto ranar Asabar ta hannun mai ba da shawara ta musamman kan sabbin kafafen yada labarai na Wamakko, Bashar Abubakar.

Abubakar ya bayyana cewa taron ya samu halartan taron ministan harkokin ‘yan sanda, Alhaji Maigari Dingyadi, dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar, Alhaji Ahmad Aliyu, da sauran fitattun ‘yan jam’iyyar APC da dama.

Ya ruwaito Alhaji Isa Sadiq-Achida, shugaban jam’iyyar APC na jihar a lokacin da yake magana a madadin jam’iyyar yana tabbatar wa sabon dan jam’iyyar da magoya bayansa cewa za su yi daidai da sauran mambobin jam’iyyar.

Ya ce, “Hakika ina da yakinin cewa sauya sheka na Bojo-Bodinga, alama ce mai kyau ga jam’iyyar APC kuma alama ce ta nasarar jam’iyyar a dukkan matakai.”

A nasa bangaren, Bojo-Bodinga, dan jam’iyyar PDP mai wakiltar mazabar Sokoto ta Kudu, ya bayyana cewa shi da jiga-jigan magoya bayansa a fadin jihar sun fice daga PDP zuwa APC.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp