Mutum aƙalla 30 ne suka mutu sannan wasu 80 suka ji raunuka sakamakon wani harin ƙunar-bakin-wake a kan masu sallar Juma’a a masallacin ‘yan Shia da ke Peshawar da ke arewacin Pakistan.
Wani da ya gane wa idonsa faruwar lamarin ya ga maharin kafin ya buɗe wa masallatan wuta, yana harbinsu ɗaya bayan ɗaya, kamar yadda kamfanin labarai na AFP ya ruwaito.
“Daga nan kuma sai ya tarwatsa kan sa,” in ji shaidar mai suna Ali Asghar.
Muhammad Ali Saif, mai magana da yawun gwamnatin yankin, ya faɗa wa AFP cewa mutum fiye da 30 aka kashe sannan aka jikkata wasu 80, yana bayyana shi da “harin ƙunar-baƙin-wake”.
Wakilin AFP ya ga gawarwakin mutane warwatse a wurin da kuma ‘yan sanda suna rarrashin ‘yan uwansu