Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta kama wani dan kungiyar Islamic State West Africa Province (ISWAP) kan fashewar wani abu a kusa da fadar Ohinoyi na Ebiraland a Okene, jihar Kogi.
An kai harin ne a ranar 29 ga watan Disamba yayin ziyarar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kai domin kaddamar da wasu ayyuka.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Peter Afunanya ya fitar a ranar Laraba ya bayyana Abdulmumin Ibrahim Otaru (aka Abu Mikdad) a matsayin wanda ya shirya.
Otaru, wanda aka bayyana a matsayin “babban kwamanda” na kungiyar ta’addanci, ko dai yana hadewa ko kuma yana da hannu a wasu hare-hare da dama.