fidelitybank

Wanda ya aikata laifi aka ce ya mutu ya sake shiga hannu a Scotland

Date:

Kotu ta yanke hukuncin cewa wani mutum da aka kama a wani asibiti a Scotland a bara, dan kasar Amurka ne mai suna Nicholas Rossi, bayan an kammala bincike. Mutumin ya yi iƙirarin cewa shi ne wanda aka yi masa kuskure, kuma ya dage cewa sunansa, Arthur Knight mai makon Nicholas Rossi.
Amma Kotun Edinburgh Sheriff shaidar yatsansa sun yi daidai da na Rossi.
Hukumomi a Amurka na neman a tasa keyar Rossi, bisa zargin fyade da cin zarafi. Ana zargin cewa ya yi karyar mutuwar na sa ne kuma daga baya ya gudu zuwa kasar Scotland, domin gujewa fuskantar tuhuma.
Ya shafe shekara guda a matsayin sunan shi Arthur Knight, kuma shi maraya ne daga Ireland wanda bai taba zuwa Amurka ba.

A dai watan Maris mai zuwa ne kotun za ta yanke hukuncin cewa za ta mika mutumin zuwa Amurka ya fuskanci hukunci ko akasin haka. A shekarar da ta gabata ne dai ‘yan sandan Scotland suka kama Rossi a wani asibiti bayan da aka gano zanen da yake a jikin hannun sa na Tatto ya yi kama da nasa a lokacin da ake bashi kulawa a asibitin bayan ya sha fama da cutar Covid 19.
Sai dai a gwajin shaidar zanen ya tsayar sa ta yi daidai da wanda ake tuhuma, kamar yadda kwararriyar mai bincike Lisa Davidson ta shaidawa kotu.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp