fidelitybank

Wanda suka kashe sojoji 17 ku mika kan ku – Kungiyar Matan Neja Delta

Date:

Kungiyoyin Matan Neja-Delta sun yi kira ga mutanen da ke da hannu wajen kashe sojoji na 181 Amphibious Division a yankin Okuama a Delta da su mika wuya ga hukumomin soja ba tare da bata lokaci ba don dawo da zaman lafiya a cikin al’ummomin da ke fama da rikici.

Wannan na zuwa ne a wata sanarwa da shugaban kungiyar kuma babban sakataren kungiyar, Mrs Augusta Wariboko da Dr Agnes Tari suka fitar ranar Juma’a a Abuja.

Sun kuma bukaci jama’a a Okuama da kewaye da su ba da hadin kai tare da baiwa jami’an tsaro muhimman bayanan da za su tabbatar da kama masu laifin.

Kungiyar ta ce jami’an sojin Najeriya sun yi sadaukarwa sosai ga kasar, inda ta ce ba su cancanci wannan mugun nufi ba.

Sun bayyana kisan a matsayin abin da ba za a amince da shi ba, kuma zai iya kawo cikas ga zaman lafiya a yankin.

Kungiyar matan ta ce sojoji sun taka rawar gani wajen samar da zaman lafiya a yankin, musamman yin amfani da hanyoyin da ba su dace ba, tana mai cewa dole ne a yi Allah-wadai da kisan ta kowace fuska.

Sun kuma bayyana goyon bayansu ga yunkurin da ake yi na cafke shugaban kungiyar da kuma mambobinsa da ke da alhakin wannan aika aika.

“Muna goyon bayan binciken da babban hafsan hafsoshin tsaron Najeriya, Janar Chris Musa ya bayar domin gano tushen matsalar.

“Yana da muhimmanci masu laifin su mika wuya ga hukumomin soji nan take.

“Muna kira ga mazauna Okuama da kewaye da su mika bayanai masu amfani ga jami’an tsaro.

“Mu mata a yankin Neja-Delta muna matukar adawa da wannan ta’asa ta ‘yan bindigar. Abin da ya faru ba ya wakiltar mutanen Neja-Delta.

Kungiyar ta kara da cewa “Muna goyon bayan abin da Gen. Musa da dakarunsa ke yi, musamman wajen magance satar mai.”

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp