fidelitybank

Wanda suka kai hari Coci za su fuskanci hukunci – Gwamnan Kaduna

Date:

Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna, a ranar Juma’a, ya yi tir da harin da aka kai a cocin Fadan Kamatan, cocin Katolika na Kafanchan, da ke karamar hukumar Zangon Kataf a jihar Kaduna.

Wani malamin darikar Katolika mai suna Naam Ngofe Danladi ya kone kurmus a lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a gidan shugaban cocin Katolika na Kafanchan da ke Fadan Kamatan a Zangon Kataf ranar Alhamis.

Gwamna Sani da yake bayyana takaicinsa kan kashe-kashen, ya sha alwashin zakulo wadanda suka aikata wannan danyen aiki tare da tabbatar da cewa sun fuskanci fushin doka.

Muhammad Lawal Shehu, Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, ya bayyana cewa an kai harin ne da nufin kunna wutar rikicin kabilanci da addini a Jihar Kaduna da kuma zagon kasa ga kokarin gwamnati na sake gina amana a cikin al’ummarta.

A cewar Gwamnan, “Na yi matukar bakin ciki da harin da aka kai a Fadan Kamatan Parish, Zangon Kataf.

“Wannan ta’addancin da ake yi wa masu bautar da ba su ji ba ba su gani ba, ba wai hari ne kawai ga al’ummar Katolika ba, a’a wani yunkuri ne na tayar da mutanenmu gaba da juna. Ba za mu amince da irin wannan ta’asa ba, kuma za mu yi iyakacin kokari wajen ganin an gurfanar da wadanda suka kai harin.”

Gwamnan ya bukaci hukumomin tsaro da su gaggauta binciki lamarin tare da tabbatar da cewa an kama wadanda suka aikata laifin tare da fuskantar fushin doka.

Ya ba da tabbacin cewa gwamnatinsa ta dauki matakan da suka dace don dawo da zaman lafiya a cikin al’ummomin da ke fama da rikici ta hanyar karfafa hadin gwiwa da hukumomin tsaro tare da sake farfado da hukumar ta Kaduna Vigilance Service (KADVS).

Hakazalika shugaban karamar hukumar Zangon Kataf Francis Sani ya bayyana alhininsa kan lamarin.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp