Kotun majistare mai zamanta a jihar Kano ta sake sauraren karar kisan da aka yi wa yarinyar nan ‘yar shekara biyar, Hanifa Abubakar, wadda kotun ta bayar da umarnin ci gaba da tsare wadanda ake zargi da kisan har zuwa 9 ga watan nan na Fabrairu 2022.
Lauyoyin gwamnati karkashin jagorancin, Barista Aisha Mahmud ne suka nemi a sake tsare mutane hudun da ake zargi har zauwa nan da mako guda, da za su gurfanar da su a wata babbar kotu da ke da hurumin sauararen kara, kasancewar kotun majistaren ba da ta hurumi.
A na zargin, Abdulmalik Tanko wanda shi ne mai makarantar su marigayiyar, tare da sauran mutum uku gaban kotun majistaren a Gidan Murtala da ke birnin na Kano, yau Laraba da laifin kisan kai.