fidelitybank

Wanda ake zargi da cin mutuncin Aisha Buhari zai tsaya a gaban kotu

Date:

A yau ne ake sa ran gurfanar da ɗalibin jami’ar da ya soki uwargidan shugaban Nijeriya, inda jami’an tsaro ke tsare da shi tsawon kwana 13 ba tare da shari’ah ba.

Zuwa yanzu babu masaniya a kan tuhume-tuhumen da hukumomi za su yi wa Aminu Adamu Mohammed, wanda aka yi zargin jami’an tsaro sun ɗauko shi ba tare da sanin hukumomin jami’arsa ba, kan umarnin Aisha Buhari.

Wannan mataki yana zuwa ne yayin da ake ci gaba da kiraye-kirayen a saki Aminu.

Ɗaiɗaikun mutane da ƙungiyoyin kare hakkin ɗan adam na ƙasashen duniya irin su Amnesty International, na ci gaba da matsa lambar cewa tsare Aminu Adamu cikin sirri ba tare da an kai shi kotu ba, abu ne da ya saɓa wa doka.

Ƙanin baban Aminu Baba Azare ya ce bayan tsare Aminu tsawon kwana 13, a ƙarshe hukumomi sun shaida musu cewa yau za a gurfanar da ɗan nasu gaban wata kotu a Abuja.

Ya ce suna fatan ganin an sake shi don ya je ya tunkari jarrabawarsa ta kammala jami’a da za a fara a makarantarsu.

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...

Daga yau wankin koda a Najeriya ya koma dubu 12 maimakon dubu 50 – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya amince da rage farashin...

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...
X whatsapp