Dan majalisa mai wakiltan yankin Kwara ta tsakiya, Sanata Ibrahim Oloriegbe, ya ce, wasu wakilai da ya baiwa kudade a lokacin zaben fidda gwani na jamâiyyar sun mayar masa da kudaden sa.
Ya bayyana haka ne a lokacin da ya fito a gidan talabijin na Channels Television na Sunrise Daily inda ya yi magana kan rikicin da ke tsakanin jamâiyyar mai mulki.
Sanata Oloriegbe ya caccaki tsarin da aka gudanar da zabukan fidda gwanin da aka fi yi a jihohin da aka fi zargin gwamnonin da dora wakilai a kan magoya bayan jamâiyyar.
âBabu wani majalisa; kamar a jiha ta, gwamna kawai ya zabo su (delegates) da daddare ya ce, mun yi primaries sai jerin suka zo. Don haka, ba ku ma san su waye wakilan baâĤ kuma hakan ya faru a jihohi da yawa, âin ji shi.
âKo a inda ake zabar mutane, ya kamata a ba su âyancin yin amfani da ikonsu ta hanyar zaben wanda suke so, amma abin ba haka yake ba. Gwamnonin sun zabo wadanda za su ba su umarni kuma wasu daga cikinsu sun yi rantsuwar kada kuriâa a inda gwamnonin ke jagorantar suâĤhaka kuma ya faru a jihar Kwara.
âA zabe na (na firamare), wakilai 17 ne suka dawo don ba ni kudi na wanda na ba su na kayan aiki; wasu kuma ba don sun ce âmuna so mu zabe ku ba, amma ba a ba mu damar kada kuriâa ba. Akwai wani abokin aikina a Kogi wanda ya ambata cewa mutane sun dawo (don mayar da kudinsa).â
Dan majalisar na cikin wasu âyan jamâiyyar da dama a majalisar dattawa da suka rasa tikitin jamâiyyarsu na neman sake tsayawa takara a cikin majalisar dokokin kasar.
Yayin da wasun su suka fice daga jamâiyyar APC, wasu kuma wadanda ba su ji dadin ci gaban da aka samu ba sun gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari domin neman sa baki.