fidelitybank

Wahalar Kudi: Gwamnatin Kebbi za ta rabawa talakawa Naira biliyan 1 da miliyan 100

Date:

Gwamnatin Jihar Kebbi ta amince da sakin naira biliyan ɗaya da miliyan dari ɗaya, domin rabawa ga jama’a saboda wahalar da ake ciki kan ƙarancin mai da kuɗi a jihar.

Sakataren gwamnatin jihar Alhaji Babale Umar-Yauri, shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da aka ba kamfanin dillancin labarai na Najeriya a Birnin Kebbi, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Sakataren ya ce za a bayar da kuɗin ba tare da ɓata wani lokaci ba, inda za a rarraba wa manoma da masu sufuri da ma’aikatan gwamnnati da kuma tallafa w ɓangaren kula da lafiya.

Ya ce daga cikin kuɗin za a bai w manoman rani naira miliyan 200 sai naira miliyan 50 ga kungiyar direbobi (NURTW) sai naira miliyan 20 ga masu haya da babur da kuma naira miliyan 10 ga masu sana’ar haya da babur mai ƙafa uku.

Alhaji Babale ya kara da cewa Gwamna Atiku Bagudu ya kuma amince da a bayar da naira miliyan 200 ga asibitoci da ƙananan cibiyoyin kula da lafiya.

Bayan wannan ya ce, gwamnatin jihar ta samar da naira miliyan 530 domin sayen buhun shinkafa dubu 15, domin sayarwa a rabin farashi ga ma’aikata.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp