Gwamnatin Jihar Kebbi ta amince da sakin naira biliyan ɗaya da miliyan dari ɗaya, domin rabawa ga jama’a saboda wahalar da ake ciki kan ƙarancin mai da kuɗi a jihar.
Sakataren gwamnatin jihar Alhaji Babale Umar-Yauri, shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da aka ba kamfanin dillancin labarai na Najeriya a Birnin Kebbi, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Sakataren ya ce za a bayar da kuɗin ba tare da ɓata wani lokaci ba, inda za a rarraba wa manoma da masu sufuri da ma’aikatan gwamnnati da kuma tallafa w ɓangaren kula da lafiya.
Ya ce daga cikin kuɗin za a bai w manoman rani naira miliyan 200 sai naira miliyan 50 ga kungiyar direbobi (NURTW) sai naira miliyan 20 ga masu haya da babur da kuma naira miliyan 10 ga masu sana’ar haya da babur mai ƙafa uku.
Alhaji Babale ya kara da cewa Gwamna Atiku Bagudu ya kuma amince da a bayar da naira miliyan 200 ga asibitoci da ƙananan cibiyoyin kula da lafiya.
Bayan wannan ya ce, gwamnatin jihar ta samar da naira miliyan 530 domin sayen buhun shinkafa dubu 15, domin sayarwa a rabin farashi ga ma’aikata.