fidelitybank

Wadanda suka kakaba mana Ganduje su na da nasani – Kwankwaso

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya sake jaddada abun da ya sha faɗa a baya cewa, wasu manya ne daga sama su ka tursasa wa al’ummar Kano gwamnan da yanzu ya ke kan mulki, Abdullahi Umar Ganduje duk da cewa ya faɗi zaɓe a 2019.

Yayin wata hira ta musamman da jaridar Punch, Kwankwaso, ya ce, ”Na tabbatar yanzu wadanda su ka yi hakan suna da na sanin abun da su ka yi wa Kano. Duk jama’ar Najeriya sun san cewa Ganduje ya fadi zaɓen nan, amma haka su ka tursasawa mafi yawan jama’a ra’ayin wadanda ba su taka kara sun karya ba, wanda shi ne babban laifin da wani zai aikata”.

Ya ƙara da cewa”Abun takaici ne yadda wasu tsiraru su ka kasa ganin abun da talakawa su ka hango wa kansu.

”Mu na da ƙarin da iya hana su abun da su ka so yi a wannan lokaci, amma sai mu ka yi la’akari da cewa idan mu ka biye musu hakan ba zai haifar da ɗa mai ido ba, domin haka mu ka bar su da aniyarsu, mu ka bi matakin shari’a, amma a nan ma a ka yi abun da a ka yi” inji Kwankwaso.

A halin da a ke ciki dai a na raɗe-raɗin sasantawa tsakanin tsohon gwamnan na Kano Rabiu Musa Kwankwaso da Ganduje, bayan ziyarar ta’aziyya da Gandujen ya kai wa Kwankwaso.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp