Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya sake jaddada abun da ya sha faɗa a baya cewa, wasu manya ne daga sama su ka tursasa wa al’ummar Kano gwamnan da yanzu ya ke kan mulki, Abdullahi Umar Ganduje duk da cewa ya faɗi zaɓe a 2019.
Yayin wata hira ta musamman da jaridar Punch, Kwankwaso, ya ce, ”Na tabbatar yanzu wadanda su ka yi hakan suna da na sanin abun da su ka yi wa Kano. Duk jama’ar Najeriya sun san cewa Ganduje ya fadi zaɓen nan, amma haka su ka tursasawa mafi yawan jama’a ra’ayin wadanda ba su taka kara sun karya ba, wanda shi ne babban laifin da wani zai aikata”.
Ya ƙara da cewa”Abun takaici ne yadda wasu tsiraru su ka kasa ganin abun da talakawa su ka hango wa kansu.
”Mu na da ƙarin da iya hana su abun da su ka so yi a wannan lokaci, amma sai mu ka yi la’akari da cewa idan mu ka biye musu hakan ba zai haifar da ɗa mai ido ba, domin haka mu ka bar su da aniyarsu, mu ka bi matakin shari’a, amma a nan ma a ka yi abun da a ka yi” inji Kwankwaso.
A halin da a ke ciki dai a na raɗe-raɗin sasantawa tsakanin tsohon gwamnan na Kano Rabiu Musa Kwankwaso da Ganduje, bayan ziyarar ta’aziyya da Gandujen ya kai wa Kwankwaso.