fidelitybank

Wadanda muka zalunta su yafe mana – Maryam Abacha

Date:

Maryam Sani Abacha, uwargidan tsohon shugaban kasa, marigayi Janar Sani Abacha, ta yi Allah wadai da karuwar kalubalen tsaro da ke addabar kasar.

Uwargidan tsohon shugaban kasar ta koka kan lamarin a wajen bikin cikarta shekaru 75 da haihuwa da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis.

Hajiya Maryam ta yi amfani da wannan damar wajen addu’ar zaman lafiya, hadin kai, bunkasar tattalin arziki da ci gaban kasa.

Sai dai ta yi kira ga shugabanni da daukacin al’ummar kasar da su ji tsoron Allah a duk harkokinsu. In ji Solacebase.

“Idan kowa zai ba da gudummawar kasonsa kuma ya zama dan kasa nagari, Najeriya za ta kasance kasa mai girma da wadata, in ji ta.

Maryam Abacha ta ce, ta yafewa duk wadanda suka yi wa iyali laifi ta wata hanya ko kuma ta daban, yayin da ta yi kira ga jama’a da su rungumi yafewa juna kuma su kasance masu rikon juna.

Ta ce, “Daya daga cikin abubuwan alheri a rayuwa shi ne mutane su rungumi ruhin gafara a tsakaninsu. Ya kamata mutane su koyi yadda ake gafarta wa juna. Gafara yana da matuƙar mahimmanci kamar yadda aka jaddada shi a cikin harsuna da addinai daban-daban. Yin afuwa yana inganta zaman lafiya tare da sauran fa’idodi,”

Maryam ta ci gaba da cewa, “Ina so in yi amfani da wannan dama wajen sanar da duk wanda ke nan da wanda ba ya nan cewa, muna godiya ga Allah Madaukakin Sarki kan duk abin da ya same mu na alheri ko mara kyau. Ina kuma son kowa ya sani na yafe wa wadanda suka zalunce mu, a lokaci guda, kuma ina son wadanda muka zalunta su yafe mana, domin Allah ya tsarkake zuciyata, kuma ina nan a raye ina godiya ga Allah Madaukakin Sarki kan hakan. Zan iya mutuwa yanzu ko gobe, ina godiya ga Allah tsawon rayuwata.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...
X whatsapp