fidelitybank

Wadanda ke cin gajiyar fadan Boko Haram ba sa son daina – Zulum

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya zargi wasu mutane da rashin son kawo karshen ayyukan ta’addancin Boko Haram saboda suna cin gajiyar lamarin.

Zulum, wanda ya bayyana hakan a wata hira da BBC Hausa, ya koka da yadda wasu mutane da ya ce suna samun riba daga rikicin Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas da tafkin Chad, ke hana a kawo karshen yaki da ‘yan ta’addan.

“Wasu ba sa son wannan rashin tsaro ya kare saboda ba za su ji dadi da hakan ba,” inji shi.

Gwamnan, wanda ya bayyana cewa an samu ci gaba a yaki da ‘yan ta’addan, ya koka da cewa yanzu ‘yan Boko Haram sun fara dawowa yankin bayan an kore su daga Chad.

Ya yi kira ga mutane su hada kai tare da goyon bayan jami’an tsaro don magance matsalar Boko Haram.

Sai dai gwamnan bai bayyana takamaiman wadanda ke cin gajiyar rashin tsaron yankin ba.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp