fidelitybank

Wadanda ba sa kishin PDP su ficce tun yanzu – Saraki

Date:

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, ya ce duk waɗanda ke da niyyar barin jam’iyyar adawa ta PDP gwamma sun fice tun yanzu domin bai wa masu kishin jam’iyyar damar sake gina ta.

Saraki ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar alhamis inda ya mayar da martani bayan wasu jiga-jigan Jam’iyyar a jihar Delta sun sanar da ficewarsu a cikin makon nan.

A ranar Laraba ne Sheriff Oborevwori, gwamnan jihar ta Delta ya bar jam’iyyar PDP ya koma jam’iyyar All Progressives Congress (APC), yayin da tsohon gwamnan jihar Ifeanyi Okowa ke shirin komawa jam’iyya mai mulki nan ba da jimawa ba.

Oborevwori ya gaji Okowa a matsayin gwamnan Delta bayan ya lashe zaɓen 2023 a ƙarƙashin inuwar P D P.

Saraki ya ce ya samu kiraye-kiraye da dama daga ƴan jam’iyyar da abin ya shafa da kuma matasa masu goyon bayan dimokraɗiyya game da rugujewar reshen jam’iyyar ta jihar Delta a kwanakin baya. “Waɗanda ke son barin PDP su bari tun yanzu, su bar sauran mu da ke son ci gaba mu mayar da hankali wajen sake gina jam’iyyar,” in ji sanarwar.

Saraki ya bayyana cewa adawa mai ƙarfi na da matukar muhimmanci ga ɗorewar dimokraɗiyya, inda ya ƙara da cewa Najeriya ba za ta iya ci gaba a matsayin ƙasa mai jam’iyya ɗaya ba.

“Don ɗorewar dimokraɗiyya, dole ne a tabbatar da cewa mutane na da zaɓin da ya dace a kowane lokaci,” in ji shi.Wan

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp