Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya ce wakar Kizz Daniel da Tekno ta 2023 mai suna ‘Buga, ta kusa zama wakar kasa ta biyu.
Da yake magana a wata hira da ya yi da tashar talabijin ta Arise TV, Shettima wanda bidiyon rawa na ‘Buga’ ya fara yaduwa a bara, ya bayyana cewa ya shiga wannan kalubalen ne saboda Najeriya na bukatar nuna fasaharta da al’adunta ga duniya.
Ya ce gwamnati na da hangen nesa mai suna “Nigeria Destination 2030” kuma ta ci gaba da jajircewa wajen inganta fasaha da al’adu domin ganin an samu babban hangen nesa.
Ya ce, “Muna da kyakkyawar manufa mai suna ‘Nigeria Destination 2030.’ Ba za mu iya guduwa daga gaskiyar cewa fasahar kere-kere da al’adun Nijeriya na haifar da tarzoma a fagen duniya ba. Kuma Najeriya ta dade da ficewa daga fagen duniya. Wannan hanya ce a gare mu don sake dawo da Najeriya. Kuma raye-rayen ‘Buga’ sun kusa zama wakar mu ta kasa ta biyu. Don haka dole ne mu nuna Najeriya.”