Hukumar raya ƙasashe ta Amurka USAID da haɗin gwiwar gidauniyar AbdulSamad Rabi’u, sun gyara cibiyoyi guda goma na kula da masu fama da tarin fuka a Najeriya.
Cibiyoyin za su taimaka wajen gwaje-gwaje don gano mutanen da suka kamu da tarin da kuma hana yaɗuwarsa a sassan ƙasar.
An raba aikin gyaran cibiyoyin kula da masu tarin fukar ne a sassan ƙasar, inda jihar Legas da Anambra da Oyo da kuma Rivers suka ci gajiya daga kudanci.
Sauran jihohin da suka amfana sun haɗar da Kano da Bauchi da kuma Katsina.
Waɗannan cibiyoyi sun samu gyara da kuma kayan aiki na zamani domin gudanar da gwaje-gwajen lafiya da kula da masu ɗauke da tarin fuka.
Najeriya wadda ke matsayi na ɗaya a jerin ƙasashen da suka fi fama da bazuwar tarin fuka a Afirika, tana fuskantar manyan ƙalubale a fannin kula da lafiya, wanda kuma ke buƙatar kulawar gaggawa.
Yanzu haka dai kusan kashi biyar na masu tarin fuka a duniya baki ɗaya, suna Najeriya.
Aƙalla mutum dubu 98 ne cutar ke kashewa duke shekara a Najeriya.
A shekarar 2022, hukumar tallafawa ƙasashe ta Amurkan ta samu tallafin dala dubu 500 daga gidauniyar AbdulSamad Rabi’u domin gudanar da ayyukan yaƙi da tarin fuka da dakile cin zarafin mata.