fidelitybank

USAID da gidauniyar Abdulsamad sun gyara cibiyoyin tarin fika

Date:

Hukumar raya ƙasashe ta Amurka USAID da haɗin gwiwar gidauniyar AbdulSamad Rabi’u, sun gyara cibiyoyi guda goma na kula da masu fama da tarin fuka a Najeriya.

Cibiyoyin za su taimaka wajen gwaje-gwaje don gano mutanen da suka kamu da tarin da kuma hana yaɗuwarsa a sassan ƙasar.

An raba aikin gyaran cibiyoyin kula da masu tarin fukar ne a sassan ƙasar, inda jihar Legas da Anambra da Oyo da kuma Rivers suka ci gajiya daga kudanci.

Sauran jihohin da suka amfana sun haɗar da Kano da Bauchi da kuma Katsina.

Waɗannan cibiyoyi sun samu gyara da kuma kayan aiki na zamani domin gudanar da gwaje-gwajen lafiya da kula da masu ɗauke da tarin fuka.

Najeriya wadda ke matsayi na ɗaya a jerin ƙasashen da suka fi fama da bazuwar tarin fuka a Afirika, tana fuskantar manyan ƙalubale a fannin kula da lafiya, wanda kuma ke buƙatar kulawar gaggawa.

Yanzu haka dai kusan kashi biyar na masu tarin fuka a duniya baki ɗaya, suna Najeriya.

Aƙalla mutum dubu 98 ne cutar ke kashewa duke shekara a Najeriya.

A shekarar 2022, hukumar tallafawa ƙasashe ta Amurkan ta samu tallafin dala dubu 500 daga gidauniyar AbdulSamad Rabi’u domin gudanar da ayyukan yaƙi da tarin fuka da dakile cin zarafin mata.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp