fidelitybank

USAID da gidauniyar Abdulsamad sun gyara cibiyoyin tarin fika

Date:

Hukumar raya ƙasashe ta Amurka USAID da haɗin gwiwar gidauniyar AbdulSamad Rabi’u, sun gyara cibiyoyi guda goma na kula da masu fama da tarin fuka a Najeriya.

Cibiyoyin za su taimaka wajen gwaje-gwaje don gano mutanen da suka kamu da tarin da kuma hana yaɗuwarsa a sassan ƙasar.

An raba aikin gyaran cibiyoyin kula da masu tarin fukar ne a sassan ƙasar, inda jihar Legas da Anambra da Oyo da kuma Rivers suka ci gajiya daga kudanci.

Sauran jihohin da suka amfana sun haɗar da Kano da Bauchi da kuma Katsina.

Waɗannan cibiyoyi sun samu gyara da kuma kayan aiki na zamani domin gudanar da gwaje-gwajen lafiya da kula da masu ɗauke da tarin fuka.

Najeriya wadda ke matsayi na ɗaya a jerin ƙasashen da suka fi fama da bazuwar tarin fuka a Afirika, tana fuskantar manyan ƙalubale a fannin kula da lafiya, wanda kuma ke buƙatar kulawar gaggawa.

Yanzu haka dai kusan kashi biyar na masu tarin fuka a duniya baki ɗaya, suna Najeriya.

Aƙalla mutum dubu 98 ne cutar ke kashewa duke shekara a Najeriya.

A shekarar 2022, hukumar tallafawa ƙasashe ta Amurkan ta samu tallafin dala dubu 500 daga gidauniyar AbdulSamad Rabi’u domin gudanar da ayyukan yaƙi da tarin fuka da dakile cin zarafin mata.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp