fidelitybank

Umarni kawai muke jira daga Tinubu mu bude iyakar Nijar da Najeriya – Kwastam

Date:

Hukamar yaƙi da fasa ƙwauri ta Kwastam, ta ce, tana jiran ta samu umarni daga gwamnati, kafin ta buɗe iyakar ƙasar da makwabciyarta Nijar.

Wannan shi ne karo na farko a hukumance da hukumar ta fito ta bayyana haka, duk da kiraye-kirayen da jama’a ke ta yi kan a bude kan iyakar.

Hukumar ta ce nan ba da wani lokaci mai tsawo ba ne ta ke sa ran za a buɗe bakin iyakar.

Ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta yamma, ECOWAS ko CEDEO ta bayyana ɗage takunkuman da ta ɗorawa Nijar, lamarin da ya kai ga rufe bakin iyakokin ƙasashen ƙungiyar da Nijar na tsawon watanni.

Tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan yulin 2023 ne Najeriya ta rufe iyakokinta da Nijar lamarin da ya haifar da ƙaruwar matsin rayuwa ga ƴan Najeriyar da kuma Nijar ɗin.

A halin yanzu akwai ɗaruruwan motocin dakon kaya ɗauke da kayan abinci da na masarufi da aka hanawa shiga Najeriyar.

Ƴankasuwar Najeriyar sun yi maraba da umarnin cire takunkumin da ECOWAS ta yi, sai dai kawo yanzu ba su samu shigo da kayan ba saboda ci-gaba da kasancewar bakin iyakar a rufe.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp