Gwamnatin Ukraine ta yi watsi da tayin da Rasha ta yi mata na bai wa mayakanta damar ficewa salin-alin daga birnin Mariupol da dakarun Rasha suka yi wa kawanya, matukar za su zubda makamansu.
Mataimakin firaminista ya ce, babu wani batu da za su aminta da shi, kawo daga ficewa da a zubda makamai.
Andrei mazaunin Mariupol ne, wanda ke haka rami don binne makwabtansa da suka mutu, ya ce, ya na fatan za a shirya yi musu jana’za, wannan ta wucin gadi ce, an kashe masu ‘yan uwa da abokan arziki.
A kullum kashe mutane ake yi a birnin nan lamarin kullum kara kazancewa ya ke.
Rasha dai ta gargadi hukumomin Ukraine cewa, za su fuskanci ruwan bama-bamai matukar ba su mika wuya ba.