fidelitybank

Ukraine za ta cigaba da fitar da kayan abinci zuwa kasashen Afrika

Date:

Ministan harkokin waje na Ukraine, Dmytro Kuleba, ya ce a shirye kasarsa take ta koma ta ci gaba da fitar da hatsi zuwa kasashen Afirka da sauran sassan duniya ba tare da wani sharadi ba, idan har Rasha ta kawo karshen rufe hanyar da ta yi ta teku ( Bahar Aswad).

A wata hira da jaridar kasar Tanzania ta, Citizen, ministan ya ce, duk da cewa kasashen Afirka da yawa sun kasance ‘yan ba-ruwanmu a yakin mamayar da Rasha ke yi da karasa, Ukraine za ta tabbatar da ci gaba da aiwatar da bangarenta na yarjejeniyar da ke tsakaninsu.

Ya ce, Ukraine, za ta ci gaba da aiki kut da kut tare da dukkanin kasashen Afirka a kwanaki da makonnin da ke tafe domin ta tabbatar dukkanin kayan abincin da aka saya sun kai ga kasuwannin kasashen.

Ta kuma yi kokarin kawo karshen karancin abincin da ake yi a duniya, wanda Rasha ta haifar, in ji shi.

Mista Kuleba ya bukaci duniya da kuma dukkanin kasashen Afirka da su yi aiki tare su matsa wa Rasha lamba ta bari a rika wucewa da kayan abinci ta ruwa zuwa kasashe.

Farashin mai da kayan abinci a Afirka ya yi tashin gwauron-zabi tun daga ranar 24 ga watan Fabrairu, lokacin da yakin Rasha da Ukraine ya barke.

Duk wani yunkuri na wasu shugabanni na sassauta lamarin wanda rikicin ya haddasa ya gagara samun nasara.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp