Hukumomi a Ukraine sun ce, sun gano wasu wurare biyu da aka binne ɗaruruwan mutane a garin Lie-man da ke gabashin ƙasar wanda dakarun Ukraine ɗin suka kwato daga na Rasha a ƴan kwanakin nan.
Wakiliyar BBC ta ce Gwamnan Yankin Donetsk, Pavlo Kirilenko, ya bayyana cewa akwai wuri ɗaya da ke da kaburburan mutum 200.
Ana kyautata zaton mutanen da ke kwance a cikin kaburburan fararen hula ne.
Ɗaya wurin da aka binne mutanen kuwa wawakeken kabari ne wanda ake kyautata zaton an zuba fararen hula da sojoji a ciki.
Tuni jami’an tsaron Ukraine suka soma bincike kan ramukan da aka gano.