fidelitybank

Ukraine ta fara ƙwace wasu yankuna da Rasha ta kama

Date:

Dakarun Ukraine na mayar wa da na Rasha martani a wasu yankunan, inda wasu rahotanni ke cewa sun ƙwace wani gari a kusa da Kyiv babban birnin ƙasar.

Mahukunta a garin Makariv da ke yamma da Kyiv sun ce tutocin Ukraine ne ke tashi a garin ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

Wani mai sharhi kan harkokin tsaro a Birtaniya ya faɗa wa BBC cewa martanin da dakarun Ukraine ke mayarwa ka iya sa Rasha ta sauya salon kai hari.

Haka ma mai magana da yawun ma’aikatar tsaron Amurka ya ce Ukraine na ƙara kama garuruwa a kudanci.

Mayaƙan sa-kai da dakarun Ukraine sun lalata wani ayarin motocin soja na Rasha a garin Voznesensk sannan suka kore su daga garin.

Haka nan, dakarun Ukraine na yunƙurin ƙwato garin Kherson wanda Rasha ta fara ƙwacewa.

Sai dai wakilin BBC a Kyiv, James Waterhouse, ya ce labarin nasarar ba wani mai girma ba ne bayan shafe kwanaki ana fafata yaƙi a wuri ɗaya da kuma ƙarin hare-hare ta sama da ruwan makaman atilare.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp