Ƙungiyar Tarayyar ƙasashen Afirka, AU ta naɗa tsohon shugaban ƙasar Kenya Uhuru Kenyatta domin ya jagoranci tawagar jami’anta da za su yi aikin sa ido a zaɓukan da ke tafe a Najeriya.
Tawagar masu sanya idon ta ƙunshi wakilan hukumoimin zaɓe na ƙasashen ƙungiyar ta AU da ƙungiyoyin farar hula da ƙwararru masu zaman kansu da kuma wasu hukumomi na ƙungiyar ta AU.
Aikin tawagar zai ƙunshi sanya ido tare da bayar da bayanai masu inganci a kan zaɓukan da kuma bayar da shawara kan yadda za a inganta zaɓen a nan gaba bisa abubuwan da suka gani.
Ana kuma sa ran tawagar ta nuna goyon bayanta da tallafa wa dorewar tsarin dumukuraɗiyya da zaman lafiya da ci-gaba a Najeriya.
A ranar 25 ga watan nan na Fabarairu ne ‘yan Najeriya za su yi zaɓen shugaban ƙasa da ‘yan majalisun dokoki na tarayya sannan kuma ranar 11 ga watan Maris su yi zaɓen gwamnoni da ‘yan majalisun dokoki na jiha.