fidelitybank

Uhuru Kanyatta zai jagoranci jami’an sanya ido a zaben Najeriya

Date:

Ƙungiyar Tarayyar ƙasashen Afirka, AU ta naɗa tsohon shugaban ƙasar Kenya Uhuru Kenyatta domin ya jagoranci tawagar jami’anta da za su yi aikin sa ido a zaɓukan da ke tafe a Najeriya.

Tawagar masu sanya idon ta ƙunshi wakilan hukumoimin zaɓe na ƙasashen ƙungiyar ta AU da ƙungiyoyin farar hula da ƙwararru masu zaman kansu da kuma wasu hukumomi na ƙungiyar ta AU.

Aikin tawagar zai ƙunshi sanya ido tare da bayar da bayanai masu inganci a kan zaɓukan da kuma bayar da shawara kan yadda za a inganta zaɓen a nan gaba bisa abubuwan da suka gani.

Ana kuma sa ran tawagar ta nuna goyon bayanta da tallafa wa dorewar tsarin dumukuraɗiyya da zaman lafiya da ci-gaba a Najeriya.

A ranar 25 ga watan nan na Fabarairu ne ‘yan Najeriya za su yi zaɓen shugaban ƙasa da ‘yan majalisun dokoki na tarayya sannan kuma ranar 11 ga watan Maris su yi zaɓen gwamnoni da ‘yan majalisun dokoki na jiha.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp