fidelitybank

Turkiyya ta kai wa ƙungiyar Kurɗawa harin ramuwar gayya

Date:

Gwamnatin Turkiyya ta ce sojojinta sun kai hari maɓoyar mayaƙan ƙungiyar Kurɗawa ta PKK masu alaƙa da Iraƙi da Siriya, bayan da aka zarge su da kai wani hari kan masana’atar jiragen sama.

A ranar Laraba ne wasu mutane biyu mace da namiji suka buɗe wuta a kusa da mashigar masana’antar, mai nisan kilomita 40 daga wajen babban birnin ƙasar Ankara, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum biyar tare da jikkata 22.

Ma’aikatar tsaron Turkiyya ta ce harin da sojojin ƙasar suka kai moɓayar mayaƙan ƙungiyar ya lalata gine-gine 47 na ƙungiyar.

Shugaban ƙasar, Recep Tayyip Erdogan ya bayyana hari kan masana’atar jiragen saman da ”abin taƙaici” a shafinsa na X.

Ministan tsaron cikin gida na ƙasar, Ali Yerlikaya ya ce ɗaya daga ckin maharan ɗan ƙungiyar PKK ne mai suna Ali Orek. In ji BBC.

Ƙungiyar Kurɗawa ta PKK, haramtacciyar ƙungiyar ce da aka bayyana da ta’addanci a Turkiyya da Amurka da Birtaniya, inda kuma take yaƙi da hukumomin Turkiyya tun shekarun 1980, kan abin da ta kira ƙwatar ‘yancin Kurɗawa marasa rinjaye a ƙasar.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp