fidelitybank

Turkiyya ta kai wa ƙungiyar Kurɗawa harin ramuwar gayya

Date:

Gwamnatin Turkiyya ta ce sojojinta sun kai hari maɓoyar mayaƙan ƙungiyar Kurɗawa ta PKK masu alaƙa da Iraƙi da Siriya, bayan da aka zarge su da kai wani hari kan masana’atar jiragen sama.

A ranar Laraba ne wasu mutane biyu mace da namiji suka buɗe wuta a kusa da mashigar masana’antar, mai nisan kilomita 40 daga wajen babban birnin ƙasar Ankara, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum biyar tare da jikkata 22.

Ma’aikatar tsaron Turkiyya ta ce harin da sojojin ƙasar suka kai moɓayar mayaƙan ƙungiyar ya lalata gine-gine 47 na ƙungiyar.

Shugaban ƙasar, Recep Tayyip Erdogan ya bayyana hari kan masana’atar jiragen saman da ”abin taƙaici” a shafinsa na X.

Ministan tsaron cikin gida na ƙasar, Ali Yerlikaya ya ce ɗaya daga ckin maharan ɗan ƙungiyar PKK ne mai suna Ali Orek. In ji BBC.

Ƙungiyar Kurɗawa ta PKK, haramtacciyar ƙungiyar ce da aka bayyana da ta’addanci a Turkiyya da Amurka da Birtaniya, inda kuma take yaƙi da hukumomin Turkiyya tun shekarun 1980, kan abin da ta kira ƙwatar ‘yancin Kurɗawa marasa rinjaye a ƙasar.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp