Kasar Turkiyya da Najeriya sun amince da wata sabuwar yarjejeniya na inganta hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya.
Sanarwar da ministan lafiya na kasar Turkiyya, Fahrettin Koca ya sanar a shafin sa na Twitter a ranar Litinin.
Ya ce, “Mun sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa a fannonin kiwon lafiya da kimiyyar likitanci tare da Ministan Lafiya na Najeriya Dr. Osagie Ehanire,” in ji Ministan Lafiya na Turkiyya Fahrettin Koca.
Koca ya kara da cewa, “An kuma sanya hannu kan yarjejeniyar jinya tsakanin ofishin jakadancin Najeriya da ke Ankara da ma’aikatar lafiya ta Turkiyya ta kasa da kasa.”