Hukumar tarrayar Turai, ta mika Yuro miliyan 102 da digo 5 a matsayin agajin jin kai, domin taimakawa al’ummomin da ba su da karfi a Najeriya, Nijar, Chadi da Kamaru, yayin da al’amuran jin kai ke ci gaba da tabarbare a yankin tafkin Chadi.
Tashe-tashen hankula a yankin, inda fararen hula ke kara fuskantar hare-haren da ake kai wa, na haifar da tarwatsa jama’a, da gurgujewar rayuwa da kuma rashin samun damar gudanar da ayyukan yau da kullum.
Hukumar ta ware Yuro miliyan 102 da digo 5 a matsayin agajin jin kai domin taimakawa al’ummomin da ba su da karfi a Najeriya, Nijar, Chadi da Kamaru, yayin da al’amuran jin kai ke ci gaba da tabarbare a yankin tafkin Chadi.
Tashe-tashen hankula a yankin, inda fararen hula ke kara fuskantar hare-haren da ake kai wa, na haifar da tarwatsa jama’a, da gurgujewar rayuwa da kuma rashin samun damar gudanar da ayyukan yau da kullum.
An yi wannan alkawarin ne a yayin taron koli na yankin tafkin Chadi, wanda aka gudanar a Yamai tsakanin ranakun 23-24 ga watan Janairu.
Za a raba jimillar adadin na shekarar 2023 kamar haka: Najeriya (miliyan 34), Nijar (miliyan 25), Chadi (miliyan 26.5) da Kamaru (€17 miliyan). Tallafin na daga cikin adadin Yuro miliyan 181.5 da aka ware a wannan shekara ga yankin tafkin Chadi, da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da kuma yankin Sahel, kamar yadda aka sanar a makon jiya.