Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar (APC) Asiwaju Bola Tinubu, zai yi jawabi a zauren majalisar wakilai na jam’iyyar APC a ranar 16 ga Maris, 2022.
A cikin wata wasika da ya sanyawa hannu da kan sa ga kakakin majalisar Femi Gbajabiamiala, wacce aka karanta wani bangare a zaman majalisar a ranar Talata, tsohon gwamnan na Legas ya nemi jama’a da mambobin su yi masu jawabi kan shirye-shiryen da yake yi wa kasa.
Daya daga cikin masu neman takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP Cif Mao Ohuanbuwa shi ma zai gana da mambobin jam’iyyar PDP a majalisar da misalin karfe 8:00 na dare ranar Talata.
Sanarwar taron da Shugaban Marasa Rinjaye, Ndudi Elumelu ya sanyawa hannu, wanda shugaban majalisar ya karanta ya nuna cewa, mai neman tsayawa takarar zai sayar da shirinsa ga ‘ya’yan jam’iyyar gabanin babban taron, domin zabar wanda zai daga tutar jam’iyyar.
Tuni dai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya yi irin wannan ganawa da kungiyoyi.