fidelitybank

Tuntubi ya rage tawagarsa zuwa taron Majalisar Ɗinkin Duniya

Date:

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya sanar da rage yawan tawagar wakilan ƙasar da za su halarci taron babban zauren Majalisar Dinkin Duniya karo na 79, da za a gudanar a birnin New York na Amurka cikin watan Satumba mai zuwa.

Shugaban ma’aikatar fadar shugaban kasar, Femi Gbajabiamila ne ya sanar da hakan ranar Asabar, lokacin wani taron bita da fadar shugaban ƙasar ta shirya wa shugabannin hukumomin gwamnati da ke ƙarƙashin kulawar fadar, kamar yadda kakakin shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale ya bayyana cikin sanarwa da ya fitar.

Gbajabiamila ya ce, Shugaba Tinubu, ya ɗauki matakin ne domin rage yawan kuɗin da gwamnati ke kashewa a lokacin tafiye-tafiyen jami’an gwamnatin.

Da yake ƙarin haske kan ƙudurin, ya ce, fadar shugaban ƙasar da hukumomin da ke ƙarƙashin kulawarta, na gudanar da ayyukansu bisa tsarin doka da ƙa’ida, da kuma bin umarnin shugaban ƙasar, Gbajabiamila ya ce, shugaban ya ɗauki matakin ne da nufin tabbatar da ingantaccen tsari wajen gudanar da gwamnatinsa.

”Na tattauna da shugaban ƙasa kan wannan, kuma ya sanar da ni cewa za mu ga haka cikin makonni masu zuwa lokacin babban taron zauren majalisar Dinkin Duniya da za a yi a birnin New York’’.

Mista Gbajabiamila ya ƙara da cewa, a lokacin zanga-zangar tsadar rayuwa da ta gabata a ƙasar, an yi maganar rage yawan kuɗin da gwamnati ke kashewa, don haka ya ce yanzu kowa na jiran ganin yawan tawagar da Najeriya za ta je da ita taron na Majalisar Dinkin Duniya.

”A baya mun sani cewa, wasu na amfani da taron wajen tafiya harkokinsu na ƙashin kai, don haka ne shugaban ƙasa ya bayar da umarnin cewa, a wannan karon duk wanda ba shi da abin yi a taron, to kada ya kuskura ya shigar tawagarmu zuwa Amurka, wannan shi ne umarnin Shugaban ƙasa’’, in shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasar.

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...
X whatsapp