fidelitybank

Tunanin El-Rufa’i ya koma kasar waje da zama bayan ya sauka – Wakilan Kaduna

Date:

Mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Kaduna, sun roki jagoran jam’iyyar na kasa kuma dan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu, da ya zabi gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a matsayin mataimakinsa a zaben shugaban kasa na 2023.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne Tinubu ya kai ziyara Kaduna, domin zayyana kuri’un wakilan jam’iyyar APC na Kaduna su 69 gabanin zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar.

Mai fatan zaman shugaban kasar ya shaida wa wakilan cewa, yana da yakinin cewa shi ne zai zama shugaban kasa a lokacin da shugaba mai ci Muhammadu Buhari ya mika ragamar mulki.

Tinubu ya ce, “Wasu suna gudu, ban san inda za su ba amma ina zuwa Villa.”

Dangane da wannan batu, wakilan PDP na Kaduna baki daya sun amince da Tinubu, yayin da jam’iyyar APC reshen Kaduna ta roki Tinubu ya zabi El-Rufai a matsayin abokin takararsa.

Da yake magana a madadin wakilan Kaduna, dan majalisar wakilai mai wakiltar Sabon Gari, mazabar Kaduna ta tarayya, kuma shugaban kwamitin majalisar wakilai mai kula da tashoshin jiragen ruwa, Garba Babawo, ya roki Tinubu da ya zabi El-rufai a matsayin mataimakinsa.

Babawo ya ce, “Muna da bukatar ka (Tinubu), yallabai. Abin da zan fada ban fada wa gwamnanmu ba, domin na san idan na fada masa ba zai goyi bayan hakan ba. Muna so ka dauki gwamnanmu a matsayin abokin takararka.

“Ba ma son ya je ya zauna a wajen kasar nan bayan zabe ,saboda mun san shirinsa. Shirinsa shi ne ya bar kasar ya zauna a ketare bayan ya kammala aikin gwamna. Amma muna son ya yi wa kasa hidima a matsayin mataimakin ku”.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp