fidelitybank

Tunanin El-Rufa’i ya koma kasar waje da zama bayan ya sauka – Wakilan Kaduna

Date:

Mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Kaduna, sun roki jagoran jam’iyyar na kasa kuma dan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu, da ya zabi gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a matsayin mataimakinsa a zaben shugaban kasa na 2023.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne Tinubu ya kai ziyara Kaduna, domin zayyana kuri’un wakilan jam’iyyar APC na Kaduna su 69 gabanin zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar.

Mai fatan zaman shugaban kasar ya shaida wa wakilan cewa, yana da yakinin cewa shi ne zai zama shugaban kasa a lokacin da shugaba mai ci Muhammadu Buhari ya mika ragamar mulki.

Tinubu ya ce, “Wasu suna gudu, ban san inda za su ba amma ina zuwa Villa.”

Dangane da wannan batu, wakilan PDP na Kaduna baki daya sun amince da Tinubu, yayin da jam’iyyar APC reshen Kaduna ta roki Tinubu ya zabi El-Rufai a matsayin abokin takararsa.

Da yake magana a madadin wakilan Kaduna, dan majalisar wakilai mai wakiltar Sabon Gari, mazabar Kaduna ta tarayya, kuma shugaban kwamitin majalisar wakilai mai kula da tashoshin jiragen ruwa, Garba Babawo, ya roki Tinubu da ya zabi El-rufai a matsayin mataimakinsa.

Babawo ya ce, “Muna da bukatar ka (Tinubu), yallabai. Abin da zan fada ban fada wa gwamnanmu ba, domin na san idan na fada masa ba zai goyi bayan hakan ba. Muna so ka dauki gwamnanmu a matsayin abokin takararka.

“Ba ma son ya je ya zauna a wajen kasar nan bayan zabe ,saboda mun san shirinsa. Shirinsa shi ne ya bar kasar ya zauna a ketare bayan ya kammala aikin gwamna. Amma muna son ya yi wa kasa hidima a matsayin mataimakin ku”.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp