fidelitybank

Tudun Biri sun rabauta da Naira miliyan 180 daga Gwamnonin Arewa

Date:

Kungiyar gwamnonin arewacin Najeriya ta bayar da tallafin naira miliyan 180 ga dagin mutanen da harin Tudun Biri ya rutsa da su.

A taron da ƙungiyar da gudanar karon farko tun bayan kafa sabuwar gwamnati

Ƙungiyar ƙarƙashin jagorancin gwamnan jihar Gombe Muhammad Inuwa Yahya, ta bayyana haka ne a lokacin taron da ta gabatar a gidan gwamnatin jihar Kaduna.

Gwamnonin sun kuma buƙaci a gabatar da cikakken bincike domin gano waɗanda ke da hannu a lamarin.

A farkon wannan wata ne dai wani jirgin sojin Najeriya maras matuƙi ya kai hari kan wasu fararen hula masu maulidi a ƙauyen Tudun Biri da ke ƙaramar hukumar Igabi a jihar Kaduna.

Lamarin da ya yi sandanin kisan aƙalla mutum 85 tare da jikkata wasu da dama.

Haka kuma gwamnonin sun jaddada ƙudurinsu na haɗin kai tsakaninsu don magance matsalar tsaro da inganta zaman lafiya da tattalin arzikin yankin, da magance matsalar rashin aikin yi, da matsalar shaye-shaye tsakanin matasa a yankin arewacin ƙasar.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp