fidelitybank

Tuchel ya zama sabon kociyan Ingila

Date:

An naɗa Thomas Tuchel a matsayin sabon kocin Ingila. Kwantiraginsa za ta fara ne daga 1 ga watan Janairun 2025.

Ɗan ƙasar Jamus mai shekara 51, ya zama mutum na uku da zai jagoranci Ingila wanda ba ɗan ƙasar ba, bayan Sven-Goran Eriksson da Fabio Capello.

Gareth Southgate ya yi murabus a watan Yuli bayan shan kashi da Ingila ta yi a hannun Sifaniya a wasan karshe na Gasar Euro 2024.

Lee Carsley, wanda aka naɗa a matsayin kocin riƙon kwarya a watan Agusta, zai ci gaba da riko a wasannin Gasar Nations League da Ingila za ta yi da ƙasashen Greece da kuma Jamhuriyar Ireland a wata mai zuwa.

Tuchel, wanda ya bar Bayern Munich a karshen kakar wasanni da ta gabata, ya ce: “Ina alfahari da wannan dama da aka ba ni na jagorantar tawagra Ingila.

“Na daɗe da son irin salon wasa da ake yi a ƙasar nan, kuma tuni na fara jin daɗin matsayi da na samu,” in ji Tuchel.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp