fidelitybank

TUC ta zargi NLC da rashin hadin kai

Date:

Kungiyar Kwadago ta TUC ta yi ikirarin cewa kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ba ta tuntube ta ba kafin ta kuduri aniyar gudanar da zanga-zangar kwanaki biyu a fadin kasar a ranakun 27 da 28 ga watan Fabrairun 2024.

Babban sakataren kungiyar Nuhu Toro a wata wasiƙa da ya aike wa shugabannin NLC ya bayyana rashin jin dadinsa kan yadda kungiyar kwadago karkashin jagorancin Joe Ajaero ba ta tuntuɓi ƙungiyar ‘yan kasuwa da Festus Osifo ke jagoranta ba kafin ta dauki matakin.

Kungiyoyin biyu dai sun bai wa gwamnati wa’adin kwanaki 14 da ta aiwatar da yarjejeniyar da suka kulla kan magance matsalar tattalin arziki da ke kara ta’azzara ƙasar, ko su tafi yajin aiki.

Tuni dai hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta buƙaci kungiyar ƙwadago ta NLC ta jingine yajin aikin da ta shirya yi ta kuma shiga tattaunawa a maimakon daukar matakan da za su iya tayar da zaune-tsaye, amma ƙungiyar da Ajaero ke jagoranta ta dage kan ci gaba da matakin da ta ɗauka na zuwa yajin aiki.

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp