fidelitybank

Tubabbun mayakan Boko Haram 559 sun yi rantsuwar mubaya’a ga gwamnati

Date:

Kimanin tubabbun ’yan Boko Haram 559 ne suka kammala karatu a shirin gwamnatin tarayya na kawar da tsattsauran ra’ayi, gyarawa da sake farfado da tinanun su (DRR).

Gwamnatin Tarayya ce ta kafa shirin na DRR a shekarar 2015, domin kawar da tunanain mayakan Boko Haram da mayar da su cikin al’umma.

Da yake jawabi a wajen taron a ranar Litinin a Gombe, Kodinetan Operation Safe Corridor, Birgediya Janar Joseph Maina, ya ce, tubabbun mayakan Boko Haram sun yi rantsuwar mubaya’a ga gwamnatin Najeriya.

Ya bayyana cewa tubabbun mayakan Boko Haram 1,070 ne aka mayar da su cikin al’umma bayan kammala karatunsu na shirin DRR.

Ya ce, tubabbun mayakan da suka kammala karatun sun isa sansanin DRR tsakanin 15 ga Yuli zuwa 6 ga Satumba, 2021.

Maina ya ce, tsaffin mayakan na Boko Haram sun gudanar da ayyukan sake gina jiki iri-iri, da suka hada da duba lafiyarsu, ba da shawara na tunani, da na motsa jiki, da ba da shawara kan shaye-shayen miyagun kwayoyi, ilimin kasashen yamma da koyar da sana’o’i.

Babban Hafsan Hafsoshin Sojin kasa, Laftanar Janar Lucky Irabor, ya bukaci tubabbun ‘yan Boko Haram da su yaba tare da mayar musu da kwarin gwiwar da aka yi musu a matsayin wadanda suka cancanci cin gajiyar shirin na DDR.

Irabor, wanda ya samu wakilcin Manjo Janar Adeyemi Yekini, ya ce, “Dole ne ku kiyaye alkawarin kasancewa masu biyayya ga gwamnatin tarayya a kowane lokaci, kuma ku guji duk wani nau’in tashin hankali da aikata laifuka.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...
X whatsapp