Kimanin tubabbun ’yan Boko Haram 559 ne suka kammala karatu a shirin gwamnatin tarayya na kawar da tsattsauran ra’ayi, gyarawa da sake farfado da tinanun su (DRR).
Gwamnatin Tarayya ce ta kafa shirin na DRR a shekarar 2015, domin kawar da tunanain mayakan Boko Haram da mayar da su cikin al’umma.
Da yake jawabi a wajen taron a ranar Litinin a Gombe, Kodinetan Operation Safe Corridor, Birgediya Janar Joseph Maina, ya ce, tubabbun mayakan Boko Haram sun yi rantsuwar mubaya’a ga gwamnatin Najeriya.
Ya bayyana cewa tubabbun mayakan Boko Haram 1,070 ne aka mayar da su cikin al’umma bayan kammala karatunsu na shirin DRR.
Ya ce, tubabbun mayakan da suka kammala karatun sun isa sansanin DRR tsakanin 15 ga Yuli zuwa 6 ga Satumba, 2021.
Maina ya ce, tsaffin mayakan na Boko Haram sun gudanar da ayyukan sake gina jiki iri-iri, da suka hada da duba lafiyarsu, ba da shawara na tunani, da na motsa jiki, da ba da shawara kan shaye-shayen miyagun kwayoyi, ilimin kasashen yamma da koyar da sana’o’i.
Babban Hafsan Hafsoshin Sojin kasa, Laftanar Janar Lucky Irabor, ya bukaci tubabbun ‘yan Boko Haram da su yaba tare da mayar musu da kwarin gwiwar da aka yi musu a matsayin wadanda suka cancanci cin gajiyar shirin na DDR.
Irabor, wanda ya samu wakilcin Manjo Janar Adeyemi Yekini, ya ce, “Dole ne ku kiyaye alkawarin kasancewa masu biyayya ga gwamnatin tarayya a kowane lokaci, kuma ku guji duk wani nau’in tashin hankali da aikata laifuka.