fidelitybank

Tsohuwar shugabar kasar Koriya ta Kudu ta shaki iskar ‘yanci

Date:

A ranar Juma’ar nan ne mahukuntar kasar Koriya ta Kudu, su ka saki tsohuwar shugabar kasar, Park Geun-hye daga gidan yari bayan da ta shafe kusan shekaru biyar, sakamakon samun ta da laifin cin hanci da rashawa, lamarin da ya janyo cece-ku-ce kan ko za ta taka wata rawa gabanin zaben shugaban kasar da za a yi a watan Maris.

Park, mai shekaru 69, ita ce shugabar kasar farko da a ka zaba, bisa tafarkin dimokuradiyya da a ka yi watsi da ita a lokacin da kotun tsarin mulkin kasar ta amince da kuri’ar da majalisar dokokin kasar ta kada a shekarar 2017 na tsige ta kan wata badakala da ta kai ga daure shugabannin wasu kamfanoni biyu na Samsung da Lotte.

Kotun kolin Koriya ta Kudu a watan Janairu ta amince da hukuncin daurin shekaru 20 a gidan yari bayan da a ka samu Park da laifin hada baki da wata kawarta, wadda ita ma ke gidan yari, domin karbar dubun dubatan biliyoyin nasarori daga kamfanonin, akasari domin biyan iyalan kawarta da ma wasu kudade masu tushen riba.

Shugaba Moon Jae-in ya yi afuwa na musamman ga Park a makon da ya gabata, ya na mai yin nuni da tabarbarewar lafiyarta da kuma bayyana fatan “cin nasara a tarihin da ya gabata da kuma inganta hadin kan kasa”.

Jami’an ma’aikatar shari’a sun kai afuwar ga Park a asibitin da ta shafe wata guda da tsakar daren ranar Alhamis, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Yonhap ya rawaito, inda ta ci gaba da zama a can har zuwa wannan lokacin.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...
X whatsapp