fidelitybank

Tsohuwar Ministan man fetur ta Najeriya ta gurfana a kotun Birtaniya

Date:

Tsohuwar ministar man fetur, Diezani Alison-Madueke, ta gurfana a gaban wata kotu da ke birnin Landan bisa zargin ta da ayyukan rashawa.

Madueke wadda ta gurfana a kotun yau Litinin, ana tuhumar ta ne da karɓar cin hanci na kuɗi da kayan ƙawa da amfani da jiragen sama na alfarma da kuma yin rayuwa irin ta hamshaƙan masu kuɗi a Birtaniya.

Ana zargin cewa ta karɓi waɗannan abubuwa ne a matsayin cin hanci domin ta bayar da kwangilolin da suka shafi man fetur.

Diezani Alison Madueke ta riƙe muƙamin minista ne ƙarƙashin mulkin tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan tsakanin shekarar 2010 zuwa 2015.

A lokacin da ta gurfana a gaban kotun a yau Litinin, ta yi magana ne kawai domin tabbatar da sunanta da kuma adireshinta.

Ba a yi mata tambaya a kan ko ta amsa laifin ko kuma a’a ba, ko da yake dai lauyanta ya shaida wa kotun cewa ba za ta amsa laifin ba.

Diezani ce ta biyu a cikin mutanen da suka taɓa riƙe wani babban muƙami a Najeriya, da suka gurfana gaban kotu a Birtaniya cikin shekarun nan bisa zargin ayyukan rashawa.

A shekara ta 2012, wata kotu a Birtaniya ta yanke wa tsohon gwamnan jihar Delta, James Ibori hukuncin ɗaurin shekara 13 bayan samun sa da laifin rashawa da halasta kuɗin haram.

A shekara ta 2015 ne aka kama Diezani Madueke a birnin Landan, jim kaɗan bayan sauka daga muƙamin minista, inda aka gurfanar da ita a kotu kan laifuka shida waɗanda suka jiɓanci rashawa.

Ta kwashe shekara takwas ɗin da suka gabata a ƙarƙashin beli a wata unguwa da ke birnin Landan.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp