fidelitybank

Tsohuwar Ministan man fetur ta Najeriya ta gurfana a kotun Birtaniya

Date:

Tsohuwar ministar man fetur, Diezani Alison-Madueke, ta gurfana a gaban wata kotu da ke birnin Landan bisa zargin ta da ayyukan rashawa.

Madueke wadda ta gurfana a kotun yau Litinin, ana tuhumar ta ne da karɓar cin hanci na kuɗi da kayan ƙawa da amfani da jiragen sama na alfarma da kuma yin rayuwa irin ta hamshaƙan masu kuɗi a Birtaniya.

Ana zargin cewa ta karɓi waɗannan abubuwa ne a matsayin cin hanci domin ta bayar da kwangilolin da suka shafi man fetur.

Diezani Alison Madueke ta riƙe muƙamin minista ne ƙarƙashin mulkin tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan tsakanin shekarar 2010 zuwa 2015.

A lokacin da ta gurfana a gaban kotun a yau Litinin, ta yi magana ne kawai domin tabbatar da sunanta da kuma adireshinta.

Ba a yi mata tambaya a kan ko ta amsa laifin ko kuma a’a ba, ko da yake dai lauyanta ya shaida wa kotun cewa ba za ta amsa laifin ba.

Diezani ce ta biyu a cikin mutanen da suka taɓa riƙe wani babban muƙami a Najeriya, da suka gurfana gaban kotu a Birtaniya cikin shekarun nan bisa zargin ayyukan rashawa.

A shekara ta 2012, wata kotu a Birtaniya ta yanke wa tsohon gwamnan jihar Delta, James Ibori hukuncin ɗaurin shekara 13 bayan samun sa da laifin rashawa da halasta kuɗin haram.

A shekara ta 2015 ne aka kama Diezani Madueke a birnin Landan, jim kaɗan bayan sauka daga muƙamin minista, inda aka gurfanar da ita a kotu kan laifuka shida waɗanda suka jiɓanci rashawa.

Ta kwashe shekara takwas ɗin da suka gabata a ƙarƙashin beli a wata unguwa da ke birnin Landan.

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp