fidelitybank

Tsohuwar Minista Uju na cigaba da baiwa EFCC hadin kai

Date:

Jami’an hukumar EFCC, mai yaƙi da cin hanci da Rashawa, sun gayyaci tsohuwar ministar mata, Uju Kennedy-Ohanenye domin amsa tambayoyi.

Kafofin yaɗa labaran Najeriya sun ce hukumar na zargin Ms Kennedy da karkatar da naira miliyan 138.4 cikin kuɗin da aka ware wa ma’aikatar a kasafin kuɗin 2023, da ɓarnatar da kuɗi da kuma saɓa ƙa’ida wajen wasu abubuwa.

Hukumar na zargin tsohuwar ministar da karkatar da kuɗin domin amfanin kanta, ciki har da kuɗaɗen da aka ware domin shirin tallafa wa mata na P-BAT.

Tsohuwar ministan ta isa harabar hukumar da safiyar ranar Alhamis, domin amsa tambayoyi, kuma bayanai na cewa har yanzu ana ci gaba da yi mata tambayoyin, kamar yadda kafofin ya da labaran ƙasar suka ruwaito.

Uju Kennedy-Ohanenye na ɗaya daga cikin ministoci biyar da Shugaban Ƙasar, Bola Tinubu ya sallama daga aiki a watan Oktoban 2024.

A watan Agustan 2023 ne shugaban ya naɗa ta a matsayin ministar kula da al’amuran matan ƙasar, matayin da ta riƙe na tsawon wata 15.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp