Tsohon shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Uche Secondus da mambobin kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2023 a jihar Ribas sun bayyana goyon bayansu ga shugaba Bola Tinubu da gwamnan jihar, Siminalayi Fubara.
Tsohon Ministan Sufuri kuma Darakta-Janar na PDP-PCC Jihar Ribas, Dr Abiye Sekibo ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Fatakwal ranar Alhamis.
Wadanda suka halarci taron sun hada da Secondus; tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilai, Austin Opara; Celestine Omehia, tsohon mataimakin gwamnan jihar, Tele Ikuru; Sanata Lee Maeba; da tsohon sakataren gwamnatin jihar Ribas, Dr. Gabriel Pidomson. da sauransu.
Majalisar ta goyi bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023, Atiku Abubakar, a zaben da ya gabata.