Allah ya yiwa tsohon shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Vincent Ogbulafor rasuwa.
Ogbulafor ya rasu ne ranar Alhamis a kasar Canada yana da shekaru 73 a duniya.
Da yake tabbatar da mutuwarsa, wani dan uwa da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, Ogbulafor ya rasu ne sakamakon rashin lafiya da ba a bayyana ba.
Marigayin shi ne sakataren jam’iyyar PDP na kasa na farko.
Ya fito daga Olokoro dake karamar hukumar Umuahia ta kudu a jihar Abia.
Ogbulafor, wanda aka haife shi a ranar 24 ga Mayu, 1949, shi ne sakataren jam’iyyar PDP na kasa na farko kafin daga bisani ya zama shugaban jam’iyyar na kasa.
Marigayin dai an tilasta masa yin murabus bayan ya yi kaca-kaca da wasu jiga-jigan PDP.
An zarge shi da laifin almundahanar kudade a lokacin da yake minista.
Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, kokarin DAILY POST na jin ta bakin Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya ci tura domin bai dauki waya ko amsa sakon da aka aika masa ba.