fidelitybank

Tsohon shugaban ma’aikatan ƙage ya yi min – Fubara

Date:

Gwamnan jihar Rivers da aka dakatar, Siminalaya Fubara ya ce, maganganun da tsohon shugaban ma’aikatan jihar, Dokta George Nwaeke ya yi a game da shi ƙage ne.

Fubara ya bayyana haka a shafukansa na sada zumunta, inda ya ce ya yi haka ne domin ya kare kansa daga zargin da aka yi masa.

“Maganar cewa wai ina shirin goyon bayan Bala Mohammed a zaɓen 2027 abin dariya ne saboda idan ma za a yi maganar, ta yaya shugaban ma’aikata zai shiga ciki, ballantana ma a ce mun zauna domin tattaunawa da ƴanbindiga masu fasa bututun mai. Wannan magana ce kawai domin babu inda aka taɓa yin zama irin wannan.”

Fubara ya ce Bala Muhammed ya kawo masa ziyara ne a matsayinsa na shugaban gwamnonin PDP, kuma a bayyane aka yi komai, kuma duniya ta gani.

“Abin ban mamaki ne Nwaeke ya yi ikirarin cewa na zauna da masu fasa bututun mai. Kowa ya san ni mutum ne mai son zaman lafiya, kuma mai kira da a zauna lafiya.

“Alamu suna nuna cewa akwai lauje cikin naɗi kan bayanan Nwaeke, kuma duk abin da yake faɗa kawai yana faɗa ne domin cika alƙawarin da ya ɗauka wa waɗanda suka biya shi, ko suka tursasa shi ya min ƙarya. Don haka nake kira ga al’ummar Najeriya, musamman ƴan jihar Rivers da su yi watsi da abin da Nwaeke ya faɗa domin ya yi haka ne domin ya ɓata min suna, sannan ya ɓata min gwamnati da ma yunƙurin shugaban ƙasa na wanzar da zaman lafiya.”

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp