fidelitybank

Tsohon shugaban ma’aikatan ƙage ya yi min – Fubara

Date:

Gwamnan jihar Rivers da aka dakatar, Siminalaya Fubara ya ce, maganganun da tsohon shugaban ma’aikatan jihar, Dokta George Nwaeke ya yi a game da shi ƙage ne.

Fubara ya bayyana haka a shafukansa na sada zumunta, inda ya ce ya yi haka ne domin ya kare kansa daga zargin da aka yi masa.

“Maganar cewa wai ina shirin goyon bayan Bala Mohammed a zaɓen 2027 abin dariya ne saboda idan ma za a yi maganar, ta yaya shugaban ma’aikata zai shiga ciki, ballantana ma a ce mun zauna domin tattaunawa da ƴanbindiga masu fasa bututun mai. Wannan magana ce kawai domin babu inda aka taɓa yin zama irin wannan.”

Fubara ya ce Bala Muhammed ya kawo masa ziyara ne a matsayinsa na shugaban gwamnonin PDP, kuma a bayyane aka yi komai, kuma duniya ta gani.

“Abin ban mamaki ne Nwaeke ya yi ikirarin cewa na zauna da masu fasa bututun mai. Kowa ya san ni mutum ne mai son zaman lafiya, kuma mai kira da a zauna lafiya.

“Alamu suna nuna cewa akwai lauje cikin naɗi kan bayanan Nwaeke, kuma duk abin da yake faɗa kawai yana faɗa ne domin cika alƙawarin da ya ɗauka wa waɗanda suka biya shi, ko suka tursasa shi ya min ƙarya. Don haka nake kira ga al’ummar Najeriya, musamman ƴan jihar Rivers da su yi watsi da abin da Nwaeke ya faɗa domin ya yi haka ne domin ya ɓata min suna, sannan ya ɓata min gwamnati da ma yunƙurin shugaban ƙasa na wanzar da zaman lafiya.”

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp