fidelitybank

Tsohon shugaban kasar Saliyo ya taho Najeriya neman lafiya

Date:

Tsohon shugaban Saliyo zai tafi Najeriya domin neman lafiya,, duk kuwa da shari’ar da yake fuskanta a ƙasar, bisa zargin hannu a yunƙurin juyin mulkin ƙasar cikin shekarar da ta gabata.

A ranar Laraba ne babbar kotun ƙasar ta bai wa Ernest Bai Koroma damar ficewa daga ƙasar na aƙalla wata uku.

To sai dai ana ganin cewa an cimma yarjejeniyar barinsa ya je zaman gudun hijira.

A watan Maris ake sa ran fara shari’ar da ake yi masa kan zargin cin amanar ƙasa.

Mista Koroma ya kwashe shekara 11 yana jagorantar Saliyo, har zuwa shekarar 2018 lokacin da aka zaɓi shugaba Julius Maada Bio a matsayin sabon shugaban ƙasar.

An ga jirgin saman shugaban Najeriya ɗauke da Mista Koroma, lokacin da yake barin filin jirgin saman birnin Freetown ranar Juma’a da rana.

Matakin na zuwa ne bayan da aka yi ta samun rahotonnin da ke cewa ƙungiyar Ecowas ta shiga tsakani domin cimma matsaya da gwamnatin Saliyo wanda ya bai wa tsohon shugaban ƙasar mai shekara 70 damar ficewa daga ƙasar.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp