fidelitybank

Tsohon shugaban kasar Saliyo ne ya kitsa juyin mulki – ‘Yan Sanda

Date:

Hukumomin tsaro a Saliyo sun ayyana tsohon shugaban ƙasar Ernest Bai Koroma a matsayin wanda ke da hannu a binciken da ake yi game da juyin mulkin da aka yi watan da ya gabata.

Mr Koroma, wanda tun ranar Asabar aka ba da shi beli, yana ƙarƙashin dokar ɗaurin talala.

Babban spetan ƴan sandan ƙasar, William Fayia Sellu ya ce Mr Koroma ba ya hannun ƴan sanda yayin da ƴan sandan ke ba shi duk girmamawar da yake buƙata.

“Hakan ba wai yana nufin ya fi ƙarfin doka bane,” in ji Mr Sellu.

Ya bayyana cewa mutum 80 da ake zargi suna hannun yan sanda kuma daga cikinsu akwai jami’an tsaro da ke aiki a yanzu da waɗanda aka kora da waɗanda suka bar aiki da farar hula da kuma wani jami’i ma’aikacin gidan yari.

An bayyana ƴar Koroma, Dankay Koroma cikin sauran mutum 54 da ake zargi a matsayin wadda ake nema ruwa a jallo, cikin jerin sunayen da ƴan sanda suka sake saki ranar Talata yayin da ake ci gaba da bincike.

Gwamnati ta yi alƙawarin ba da tagomashi ga duk wanda ya taimaka da wani bayani da zai kai ga kama waɗanda ake zargin da a yanzu ake neman su ruwa a jallo.

A makon da ya gabata ne Mr Koroma ya ce zai ƙyale doka ta yi aikinta.

Ƙungiyar Ecowas ta amince da tura sojoji zuwa ƙasar ta Saliyo.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp