Tsohon shugaban Jami’ar jihar Gombe GSU Kashere, Farfesa Abdullahi Mahadi ya mutu.
Mahadi wanda ya tb zama shugaban Jami’ar Ahmadu Bello Zaria, da ke Jihar Kaduna ya mutum yana a ranar Juma’a yana da shekara 77.
Gwamnan Jihar Gombe Inuwa Yahaya ya aike da ta’aziyyarsa ga iyalan mamacin da kuma sauran al’ummar jihar a matsayinsa na shugaban Jami’ar ta Gombe.
Tuni manyan da fitattun mutane suka rika aike ta’aziyarsu ga iyalan Farfesa Abdullahi Mahadi.