fidelitybank

Tsohon shugaban hukumar ƙwallon ƙafar Afrika Isah Hayatou ya rasu

Date:

Marigayin wanda dan kasar Kamaru ne ya shafe shekaru 29 yana shugabancin hukumar gudanarwar ta nahiyar Afirka, inda ya karbi ragamar shugabancin hukumar ta CAF a shekarar 1988, ya kuma sauka a shekarar 2017.

Ya kuma rike manyan mukamai a hukumar kwallon kafa ta Fifa.

Hayatou ya kasance mamba a kwamitin zartarwa na hukumar ta Fifa wadda ofishinta ke kasar Switzerland, daga 1990 zuwa 2017.

Ya dan yi aiki a matsayin shugaban Fifa na riko tsakanin 2015 zuwa 2016 bayan da aka dakatar da Sepp Blatter.

A sakon da ya wallafa a shafinsa na Instagram Shugaban Fifa Gianni Infantino ya jinjinawa marigayi Hayatou, wanda a lokacin kuruciyarsa dan wasan tsere ne kuma dan wasan kwallon kwando.

‘’Ina bakin ciki da jin rasuwar tsohon shugaban Caf, tsohon shugaban Fifa na rikon kwarya, mataimakin shugaban Fifa kuma dan majalisar Fifa, Issa Hayatou’’ in ji Infantino.

‘’Mutum ne mai sha’awar wasanni, ya sadaukar da rayuwarsa wajan kula da harkokin wasanni”

“A madadin Fifa, ina mika ta’aziyya ga iyalansa, abokansa, tsoffin abokan aikinsa da duk wadanda suka san shi, Allah ya sa ya huta’’.

Shi ma shugaban hukumar CAF Dr Patrice Motsepe ya mika sakon ta’aziyarsa ga iyalan marigayin

‘’Ina mika ta’aziyyata da ta’aziyyar gamayyar kungiyoyin CAF su 54, bisa rasuwar tsohon shugaban CAF, Shugaba Issa Hayatou; ga danginsa, da hukumar kwallon kafa ta kasar Kamaru da alummar kasar bakidaya’’

‘’Hukumar CAF da fanin Kwallon Kafa na Afirka za su ci gaba da gode wa Shugaba Hayatou saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar, tsawon shekaru da dama don ci gaban kwallon kafa a Afirka. Zai ci gaba da kasancewa a zukatanmu da tunaninmu har abada” in ji shi

Shugaba Motsepe ya bukaci a saukar da tutocin CAF da tutocin dukkan mambobin hukumar ta CAF kasa -kasa na tsawon kwanaki biyar domin nuna alhinin mutuwarsa.

A watan Agustan 2021 Fifa ta dakatar da Hayatou na tsawon shekara guda saboda saba ka’idojinta lokacin da ya kulla yarjejeniya mafi girma kan harkar kwallon kafar Afirka da kamfanin yada labarai na Faransa Lagardere a 2016.

Sai dai Kotun sauraren kararrakin wasanni ta soke hukuncin a watan Fabrairun shekarar 2017

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp