fidelitybank

Tsohon shugaban hukumar ƙwallon ƙafar Afrika Isah Hayatou ya rasu

Date:

Marigayin wanda dan kasar Kamaru ne ya shafe shekaru 29 yana shugabancin hukumar gudanarwar ta nahiyar Afirka, inda ya karbi ragamar shugabancin hukumar ta CAF a shekarar 1988, ya kuma sauka a shekarar 2017.

Ya kuma rike manyan mukamai a hukumar kwallon kafa ta Fifa.

Hayatou ya kasance mamba a kwamitin zartarwa na hukumar ta Fifa wadda ofishinta ke kasar Switzerland, daga 1990 zuwa 2017.

Ya dan yi aiki a matsayin shugaban Fifa na riko tsakanin 2015 zuwa 2016 bayan da aka dakatar da Sepp Blatter.

A sakon da ya wallafa a shafinsa na Instagram Shugaban Fifa Gianni Infantino ya jinjinawa marigayi Hayatou, wanda a lokacin kuruciyarsa dan wasan tsere ne kuma dan wasan kwallon kwando.

‘’Ina bakin ciki da jin rasuwar tsohon shugaban Caf, tsohon shugaban Fifa na rikon kwarya, mataimakin shugaban Fifa kuma dan majalisar Fifa, Issa Hayatou’’ in ji Infantino.

‘’Mutum ne mai sha’awar wasanni, ya sadaukar da rayuwarsa wajan kula da harkokin wasanni”

“A madadin Fifa, ina mika ta’aziyya ga iyalansa, abokansa, tsoffin abokan aikinsa da duk wadanda suka san shi, Allah ya sa ya huta’’.

Shi ma shugaban hukumar CAF Dr Patrice Motsepe ya mika sakon ta’aziyarsa ga iyalan marigayin

‘’Ina mika ta’aziyyata da ta’aziyyar gamayyar kungiyoyin CAF su 54, bisa rasuwar tsohon shugaban CAF, Shugaba Issa Hayatou; ga danginsa, da hukumar kwallon kafa ta kasar Kamaru da alummar kasar bakidaya’’

‘’Hukumar CAF da fanin Kwallon Kafa na Afirka za su ci gaba da gode wa Shugaba Hayatou saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar, tsawon shekaru da dama don ci gaban kwallon kafa a Afirka. Zai ci gaba da kasancewa a zukatanmu da tunaninmu har abada” in ji shi

Shugaba Motsepe ya bukaci a saukar da tutocin CAF da tutocin dukkan mambobin hukumar ta CAF kasa -kasa na tsawon kwanaki biyar domin nuna alhinin mutuwarsa.

A watan Agustan 2021 Fifa ta dakatar da Hayatou na tsawon shekara guda saboda saba ka’idojinta lokacin da ya kulla yarjejeniya mafi girma kan harkar kwallon kafar Afirka da kamfanin yada labarai na Faransa Lagardere a 2016.

Sai dai Kotun sauraren kararrakin wasanni ta soke hukuncin a watan Fabrairun shekarar 2017

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp