fidelitybank

Tsohon shugaban EFCC Lamorde ya rasu

Date:

Tsohon shugabana Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Najeriya, EFCC, Ibrahim Lamorde ya rasu.

Wata majiya mai kusanci da Lamorden ta tabbatar wa BBC labarin rasuwar tasa a ƙasar Masar inda yake jinyar wata rashin lafiya.

Tsohon mataimakin Sifeton ‘yan sandan Najeriyar, mai shekara 61, ya jagoranci hukumar EFCC daga shekarar 2011 zuwa 2015.

Da farko tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan ne ya naɗa shi a matsayin shugaban riƙo na hukumar a watan Nuwamban 2011, bayan sauke Farida Waziri.

Sai kuma a watan Fabrairun 2012, Mista Jonathan ya tabbatar da shi a matsayin cikakken shugaban hukumar bayan amincewar majalisar dattawan ƙasar.

Ibrahim Lamorde – ɗan asalin jihar Adamawa – ya kasance mutum na uku a jerin waɗanda suka jagoranci hukumar EFCC tun bayan kafuwarta.

A shekarar 2015 ne wani kwamitin Majalisar Dattawan Najeriya ya ƙaddamar da bincike kan zargin karkatar da dala biliyan biyar, da wasu kadarori da EFCC ta ƙwato a lokacin da yake jagorantar hukumar.

To sai dai a lokacin Ibrahim Lamorde ya musanta zargin yana mai cewa shure-shure ne kawai, kasancewar a lokacin EFCC ta gurfanar da mutumin da ya yi zargin.

A watan Nuwamban 2015 ne, tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya sauya shi da Ibrahim Magu.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp