Mutanen biyu sun kai ziyarar ce a ranar Juma’a, kwanaki bayan harin da sojojin Najeriya suka kai a ƙauyen ‘bisa kuskure.’

A ranar Lahadin da ta gabata ne wani jirgi maras matuƙi mallakin sojojin Najeriya ya harba bam sau biyu a kan masu bikin Maulidi a ƙauyen.

Tun farko hukumomi sun bayyana cewa mutum 85 ne suka rasa rayukansu a sanadiyyar harin.
Amma daga baya rundunar sojojin ƙasa ta Najeriyar ta ce mutum 81 ne harin ya hallaka.

Sai dai al’ummar ƙauyen da kuma wasu ƙungiyoyi sun bayyana cewa yawan waɗanda suka mutu sanadiyyar harin sun zarce alƙaluman da hukumomi suka bayar.

Tuni dai rundunar sojojin Najeriya ta nemi afuwa game da harin, kuma hukumomi sun ce za su biya diyya.
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i da Khalifar Tijjaniyya a Najeriya, Muhammadu Sanusi II sun kai ziyara garin Tudun Biri da ke ƙaramar hukumar Igabi a jihar Kaduna.