fidelitybank

Tsohon Sarkin Kano da tsohon Gwamnan Kaduna sun kai ziyara Tudun Biri

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i da Khalifar Tijjaniyya a Najeriya, Muhammadu Sanusi II sun kai ziyara garin Tudun Biri da ke ƙaramar hukumar Igabi a jihar Kaduna.

Mutanen biyu sun kai ziyarar ce a ranar Juma’a, kwanaki bayan harin da sojojin Najeriya suka kai a ƙauyen ‘bisa kuskure.’

..

A ranar Lahadin da ta gabata ne wani jirgi maras matuƙi mallakin sojojin Najeriya ya harba bam sau biyu a kan masu bikin Maulidi a ƙauyen.

..

Tun farko hukumomi sun bayyana cewa mutum 85 ne suka rasa rayukansu a sanadiyyar harin.

Amma daga baya rundunar sojojin ƙasa ta Najeriyar ta ce mutum 81 ne harin ya hallaka.

..

Sai dai al’ummar ƙauyen da kuma wasu ƙungiyoyi sun bayyana cewa yawan waɗanda suka mutu sanadiyyar harin sun zarce alƙaluman da hukumomi suka bayar.

...

Tuni dai rundunar sojojin Najeriya ta nemi afuwa game da harin, kuma hukumomi sun ce za su biya diyya.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp